Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-07-24 11:17:06    
Gwamnatin kasar Isra'ila ta bayyana goyon baya za a girke sojojin kasashen duniya a yankin dake kudancin Lebanon

cri

Wakilin Rediyon kasar Sin ya aiko mana labari cewa , a ran 23 ga watan nan , Ehud Olmert , firayin ministan kasar Isra'ila ya bayyana cewa , gwamnatinsa a shirye take za a kafa wata rundunar sojojin kasashen Kungiyar Turai a kudancin yankin kasar Lebanon .

A wannan rana Mr. Olmert ya gana da Frank Steinmeier , ministan harkokin waje na kasar Jamus , inda ya ce , wannan rundunar sojojin kasashen duniya ya kamata ta girke a iyakar tsakanin kasar Isra'ila da Lebanon , kuma dole ne ta iya mallake hanyar mai sada Kasar Syria da Lebanon .

A wannan rana , Josh Bolten , Direktan Ofishin Fadar gwamnatin kasar Amurka ya bayyana cewa , kasarsa tana goyon bayan irin wannan rundunar sojojin , amma sojojin kasar Amurka ba za su shiga ciki ba .

Bisa labarin daban da aka bayar , an ce , Nabih Barri , shugaban Majalisar kasar Lebanon ya ce , jam'iyyar Hezbollah tana goyon bayan kudurin gwamnatin kasar Lebanon. (Ado)