Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-07-18 21:09:28    
Ministar harkokin waje ta kasar Isra'ila ta nuna ahabaice cewa, Isra'ila ba za ta yi adawa da girke sojojin kiyaye zaman lafiya a kudancin kasar Lebanon ba

cri

A ran 18 ga wata, ministar harkokin waje ta kasar Isra'ila Tzipi Livni ta ta nuna ahabaice cewa, domin daidaita rikicin da ake yi a tsakanin Isra'ila da Lebanon, Isra'ila ba za ta yi adawa da girke sojojin kiyaye zaman lafiya a kudancin kasar Lebanon ba.

A ran nan a birnin Kudus, Malama Livni ta yi shawarwari da kungiyar da ke da mutane 3 ta MDD. Ta ce, makasudi na karshe na Isra'ila shi ne sojojin gwamnatin Lebanon su girke a kudancin Lebanon domin hana dakarun kungiyar Hezbullah su kai farmaki a kan Isra'ila. Amma sabo da a halin yanzu gwamnatin Lebanon ba ta da irin wannan kwarrewa, shi ya sa Isra'ila take son yin la'akari a kan sauran hanyoyi. Malama Livni ta ce, wannan bai bayyana cewa Isra'ila za ta rage matakin soja da take dauka a kan kungiyar Hezbullah a halin yanzu ba, dalilin da ta yi haka shi ne domin hana sake faruwar rikici tsakaninsu.

Mamban kungiyar da ke da mutane 3 ta MDD kuma manzon musamman na MDD mai kula da al'amuran shiyyar gabas ta tsakiya Terje Roed-Larsen ya ce, ya zama tilas a kafa wani tsarin siyasa domin sa kaimi ga bangarorin biyu da su daina rikicin.(Danladi)