Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-06-21 11:11:29    
Kasar Iran tana shirin yin shawarwari da kasashen duniya a kan matsalar nukiliyarta

cri

A ran 20 ga wata a birnin Baku, babban birnin kasar Azerbaijan, ministan harkokin waje na kasar Iran Manouchehr Mottaki ya bayyana cewa, kafin kasar Iran ta ba da amsa ga sabon shirin da kasashe 6 suka yi wato Amurka da Rasha da Sin da Britaniya da Faransa da Jamus, kasar Iran tana shirin yin shawarwari da kasashen duniya a kan matsalar nukiliyarta ba tare da sharadi ba.

A ran nan a birnin Moscow, shugaban kasar Rasha Putin ya yi imani cewa, za a iya janye takardar matsalar nukiliya ta Iran daga kwamitin sulhu na MDD, haka kuma za a iya sake mayar da ita zuwa hukumar makamashin nukiliya ta duniya.

A ran nan a birnin Washington , mataimakin kakakin majalisar ta kasar Amurka Adam Ereli ya ce, a kan matsalar nukiliya ta kasar Iran, kasashen Amurka da Italiya suna da ra'ayi daya, kuma suna goyon baya ga sabo shiri da kasashe 6 suka yi.(Danladi)