Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-06-17 21:57:06    
Firaministan kasar Sin ya isa birnin Alkahira don yin ziyara a kasar Masar

cri

Bisa gayyatar da takwaransa na kasar Masar Ahmed Nazif ya yi masa, firaministan kasar Sin, Wen Jiabao ya isa birnin Alkahira a ran 17 ga wata da yamma, agogon wurin, kuma ya fara yin ziyarar aiki ta sada zumunta a Masar.

A cikin jawabin da ya bayar a rubuce a filin jirgin sama na Alkahira, Mr.Wen ya ce, a halin yanzu dai, ana fuskantar sabon zarafi a wajen bunkasa huldar da ke tsakanin Sin da Masar, yin kokarin inganta huldar hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare ya dace da babbar moriyar kasashen biyu da ta jama'arsu, haka kuma zai amfana wa zaman lafiya da bunkasuwar shiyya shiyya da na duk duniya baki daya.

An ce, a lokacin ziyarar, Mr.Wen zai gana da shugaban Masar Hosni Mubarak da firaministan kasar Ahmed Nazif da dai sauran kososhin kasar, inda za su yi musanyar ra'ayoyi a kan bunkasuwar huldar da ke tsakanin bangarorin biyu a nan gaba da batutuwan da suke daukar hankulansu duka.(Lubabatu Lei)