Ba da dadewa ba, sai ya ga wata budurwa mai kyaun gani. Ta shiga gidansa kai tsaye, ta fara aikin gida. Ganin haka, Niu Lang ya fito daga wurin da ya buya, ya tambaye ta cewa, 'An gaishe ki budurwa mai kyaun gani, me ya sa kike taimako ni wajen aikin gida ?' Budurwar ta razana, kuma ta ji kunya. Ta yi magana da karamar murya, ta ce, 'Sunana Zhi Nu. Na ga kana zama cikin kadaici da shan wahala, shi ya sa na zo taimake ka.' Niu Lang ya ji murna kwarai da gaske, sai ya ce, ' Sai ki aure ni, bari mu yi aiki tare da zama tare, mu debe wa juna kewa.' Zhi Nu ta yarda. Daga baya, Niu Lang da Zhi Nu sun yi aure sun zama miji da mata. Ko wace rana, Niu Lang ya je aiki a cikin gona, Zhi Nu sai ta yi aikin saka a cikin gida. Bayan shekaru, sun haifi yara 2, namiji daya, mace daya. Suna jin dadin zamansu.
Suna nan cikin halin, sai wata rana, ana iska kuma ana hadari a can sama. Aljanu biyu sun sauka daga sama, sun zo gidan Niu Lang. Sun sanar da shi cewa, Zhi Nu jika ce ta sarkin aljanu. Shekarun da suka wuce ta bar gida ba tare da izini ba, daga baya sarkin aljanu na ta kokarin nemanta. Daga baya, aljanun 2 sun kama Zhi Nu, sun kai ta sama.
Niu Lang ya rungume yaransa, yana bakin ciki kwarai. Ya lashi takobin cewa zai nemi matarsa, da kuma dawo da ita gida. Amma, yaya mutum zai iya hawa can sama ?
1 2 3
|