Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-04-27 18:00:13    
Hu Jintao ya gana da shugabannin majalisun dokokin kasar Najeriya

cri
A ran 27 ga wata, bi da bi ne shugaba Hu Jintao na kasar Sin wanda ke yin ziyara a kasar Najeriya ya gana da shugaba Menechukwu Nnamani na majalisar dattijai ta kasar Najeriya da shugaba Aminu Masari na majalisar wakilan dokokin kasar Najeriya, inda bangarorin biyu suka yi musayar ra'ayoyi kan yadda za a kara raya dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu da kara yin musanye-musanye a tsakanin majalisun dokokin kasashen biyu.

Mr. Hu ya ce, bangaren kasar Sin yana mai da hankali sosai kan yadda za a raya dangantakar da ke tsakanin Sin da Najeriya. Yana fatan majalisun dokokin kasashen biyu za su ci gaba da yin hadin guiwa da kara yin mu'ammala a tsakanin ma'aikatansu.

Shugabannin majalisun dokokin kasar Najeriya sun bayyana cewa, dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu na ta samun karfafuwa a cikin 'yan shekarun nan da suka wuce, yanzu irin wannan dangantaka tana cikin hali mai kyau a tarihi. Hadin guiwar tattalin arziki a tsakaninsu za ta kawo wa jama'ar kasashen biyu da jama'ar kasashen yammacin Afirka fatan alheri. (Sanusi Chen)