Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-04-22 17:12:36    
Shugaban kasar Sin Mr Hu Jintao ya fara yin ziyarar aikinsa a kasar Saudiyya

cri
Bisa gayyatar da Abdullah Bin Abdul-Aziz, sarkin daular mulukiya ta Saudiyya ya yi masa ne, Mr Hu Jintao, shugaban kasar Sin ya sauka birnin Riyadh a ran 22 ga wata da safe (Agogon Saudiyya) don fara yin ziyarar aikinsa na kwanaki biyu a kasar Saudiyya.

Bayan saukarsa a filin jirgin sama, Mr Hu Jintao ya yi jawabi a rubuce cewa, tun bayan da aka kulla huldar diplomasiya a tsakanin Sin da Saudiyya a shekarar 1990, ana ta yalwata huldar nan da ke tsakanin kasashen biyu cikin kwanciyar hankali, kuma an sami kyakkyawan sakamako wajen yin hadin guiwar tsakanin kasashen biyu a fannin siyasa da tattalin arziki da ciniki da kuma al'adu da dai sauransu. Bangaren Sin yana nuna gamsuwa ga wannan. Kasar Sin tana dora matukar muhimmanci ga yalwata hulda a tsakaninta da Saudiyya, tana son yin kokari tare da bangaren Saudiyya don kara dankon aminci a tsakaninsu da kuma kara karfin hadin guiwarsu.

A lokacin ziyararsa, Mr Hu Jintao zai yi shawarwari a tsakaninsa da Abdullah, sarkin kasar Saudiyya, kuma zai gana da sauran shugabannin kasar don musaya ra'ayoyinsu a kan hulda a tsakanin Sin da Saudiyya da matsalolin kasa da kasa da na shiyya-shiyya da ke jawo hankulansu duka. (Halilu)