Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-11-03 11:09:44    
Kungiyar addinin runkunin Maronite ta kasar Lebanon ta bayyana cewa yanzu bai kamata a tattauna matsalar yin murabus na shugaba Emile Lahoud ba

cri
Wakilin Rediyon kasar Sin ya ruwaito mana labari cewa , a ran 2 ga watan nan , Kungiyar addinin runkunin Maronite ta kasar Lebanon ta bayar da sanarwa , inda ta bayyana cewa yanzu bai kamata a tattauna matsalar yin murabus na shugaba Emile Lahoud ba .

Bayan da kungiyar ta yi taro a birnin Berut wannan rana ta bayar da sanarwa cewa , kudurin 1636 da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas kwanan baya mai hadari ne , kuma za ta kawo mugun tasiri ga halin da wannan shiyya ke ciki yanzu . Sanarwar ta yi gargadin cewa , tattauna matsalar yin murabus na shugaba Emile Lahoud zai sa kasar Lebanon ta shiga cikin halin hatsari , kuma zai lahanta tattalin arzikin kasar . Sanarwar ta yi kira ga bangarori daban daban da su girmama tsarin mulkin kasar kuma su kiyaye kwarjinin shugaban kasar . (Ado)