Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-10-24 18:34:00    
Kasar Nijeriya za ta soma zaman makoki saboda mutanen da suka rasu a cikin hadarin faduwar jirgin sama

cri
A ran 24 ga wata gwamnatin kasar Nijeriya ta shelanta cewa, tun daga wannan rana ne za a soma zaman makoki saboda mutanen da suka rasu a cikin hadarin faduwar jirgin sama da ta auku a ran 22 ga wata da dare har na tsawon kwanaki 3.

Lokacin da ake zaman makokin, za a saukar da tutar Nijeriya kasa kasa, kuma za a shirya wasu bukukuwa domin addu'a. Shugaba Olusegun Obasanjo na kasar Nijeriya ya yi kira ga jama'a da su yi addu'a don mutane wadanda suka rasu a cikin hadarin da iyalansu.

A ran 22 ga wata da dare, wani jirgin saman fasinja kirar Boeing 737 na kamfanin Bellview mai zaman kansa ya fadi a wurin da ke da nisan kilomita 30 daga filin jirgin sama na Murtala Mohammed na Lagos. Mutane 117 ciki har da ma'aikata 6 na jirgin saman dukkansu sun rasu.

Yanzu, hukumar Nijeriya da abin ya shafa tana binciken dalilin da ya sa aukuwar hadarin kuma tana yin aikin tantance asalin mutanen da suka rasu a cikin hadarin. (Sanusi Chen)