Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-06-24 16:56:18    
'Yan majalisar dokokin kasar Afirka ta Kudu 5 sun yi murabus

cri
A ran 23 ga wata, 'yan majalisar dokokin kasar Afirka ta kudu 5 wadanda ake zarginsu da hannu a cikin wata matsalar rashawa sun yi murabus daga mukamansu. Sabo da haka, sun zama sauran manyan 'yan siyasa bayan tsohon shugaba Jacob Zuma na kasar wadanda kura ta rutsa da su a cikin aikin kawar da rashawa da al'amubazzaranci.

Wadannan 'yan majalisar dukkansu membobin jam'iyyar babban taro na jama'ar Afirka na Afirka ta Kudu. Kakakin jam'iyyar ya ce, yanzu wadannan 'yan majalisar suna jin kunya domin abubuwan da suka yi sun yi mummunar tasiri ga majalisar dokokin kasar da jam'iyyar da suke ciki. Ko da yake sun yi murabus daga mukaminsu, amma, dole ne za a yanke musu hukunci bisa dokoki. (Sanusi Chen)