Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-06-24 09:17:11    
Kasar Aljeriya tana son maido da dangantakar abuta da ke tsakaninta da kasar Morocco

cri
A ran 23 ga wata a birnin Algeirs, babban birnin kasar Aljeriya, ministan gudanarwa kuma ministan harkokin waje na kasar Muhammad Bedjaoui ya bayyana cewa, kasar Aljeriya tana son kwantar da kura a tsakaninta da Morocco, kuma tana son maido da dangantakar abuta da ke tsakaninta da kasar Morocco.

A gun taron manema labaru da aka shirya a ran nan, Mr Bedjaoui ya ce, kasar Aljeriya tana son bunkasa dangantakar da ke tsakaninta da kasar Morocco, bai kamata a yi la'akari da tasirin da kungiyar kawancen jama'ar yammacin Sahara ta yi musu ba. Haka kuma ya yi kira ga kasashen biyu da su kawar da bambancin ra'ayoyinsu domin kago sharadi ga ganawar da shugabannin kasashen suka yi wa juna.(Danladi)