Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-05-27 17:50:38    
Kenya ta yi fatan kafofin watsa labaru na kasar Sin za su ba da babban taimako a wajen watsa labarun Afrika

cri

Wakilin Kamfanin dillancin labarun Xinhua ya ruwaito mana labari cewa , a ran 26 ga watan nan Jorge Opio , shugaban Hukumar watsa labaru ta kasar Kenya kuma shugaban Kamfanin dillancin labaru na kasar ya ce , lokacin da kafofin watsa labaru na kasashen yamma suke watsa labarun Afrika , su kan lura da abubuwa marasa kyau kuma su kan habaka girman tasirinsu . Ya yi fatan kafofin watsa labaru na kasar Sin za su ba da babban taimako a wajen watsa labarun Afrika , ta yadda za a sa kasashen duniya su gane yalwatuwa da ci gaban kasashen Afrika kuma su ba da taimako ga kasashen Afrika a wajen fid da kai daga tasiri maras kyau wanda labarun da kasashen Yamma suka watsa bisa rashin adalci suka kawo .

A wannan rana Mu'atu , kakakin gwamnatin kasar Kenya ya ce , kafofin watsa labaru ba kawai suna watsa labarun Afrika cikin rashin adalci ba , har ma suna yin haka kan kasashe matasa masu yawa . (Ado)