Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-05-06 16:14:30    
An bukaci Nijeriya da ta mika Charles Taylor ga kotun musamman na MDD da ke kasar Saliyo

cri

Ran 4 da dare, kotun musamman na MDD da ke kasasr Saliyo ya bayar da wata sanarwa a kan shafin internet nasa, inda aka bukaci kasar Nijeriya da ta mika wa kotun Charles Taylor, tsohon shugaban kasar Liberia, wanda ke gudun hijira a kasar Nijeriya.

Cikin sanarwar, an ce, Mista Taylor yana da allaka da kungiyar al-Qaeda, kuma yana yunkurin ta da hargitsi a yammacin Afirka, bai kamata ba kasar Nijeriya ta ci gaba da bayar masa taimako. Har wa yau kuma, kotun musamman ya yi kira ga shugaba Bush na kasar Amurka da shugaba Obasanjo na kasar Nijeriya da su sake yin la'akari kan batun mika Mista Taylor ga kotun, a yayin da suke ganawa a birnin Washington a ran 5 ga wata. (Bello)