Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-26 18:08:21    
Shugaba Lien Chan na Jam'iyyar KMT ta kasar Sin ya kawo ziyara a nan babban yankin kasar

cri

Wakilin Rediyon kasar Sin ya ruwaito mana labari cewa , a ran 26 ga watan nan Shugaba Lien Chan na Jam'iyyar KMT ta kasar Sin da 'yan kungiyarsa sun isa birnin Nanjing na babban yankin kasar daga Taiwan ta hanyar Hongkong don yin ziyara cikin kwanaki 8 .

Mr. Lien ya kawo ziyara ne a babban yankin bisa gayyatar da kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta Sin da babban sakatare Hu Jintao na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin suka yi masa . Kafin shekaru fiye da 50 , Jam'iyyar KMT ta ci hasara a cikin yakin basasa kuma ta yanye jiki daga babban yankin zuwa Taiwan . Ziyarar da Mr. Lien yake yi a wannan karo ta sa Mr. Lien ya zama shugaba na farko na Jam'iyyar KMT a cikin shekaru fiye da 50 da suka wuce . ( Ado)