
Wakilin Kamfanin dillacin labarun Xinhua ya ruwaito mana labari cewa , a ran 29 ga watan nan da karfe 10 na safe , kungiyar wakilan Jam'iyyar Guomindang ta kasar Sin a karkashin jagorancin Jiang Binkun, mataimakin shugaban Jam'iyyar, a karo na farko ta kai ziyara a kabarin mazajen jiya 72 na Huanghuagang dake birnin Guangzhou.

Bayan da suka ba da sadakarwa ga mazajen jiya , Mr. Jiang ya karbi ziyarar da manema labaru suka yi masa, inda ya bayyana cewa , saboda mazajen jiya sun sadakar da ransu, shi ya sa gabobi biyu na Zirin Taiwan suka sami yalwatuwar tattalin arziki da zaman al'umma. Ya kamata mu nuna girmamawa ga wadannan masu juyin juya hali . (Ado)
|