Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-03-28 21:54:52    
Mataimakin shugaban jam'iyyar KMT ta Taiwan ya fara yin ziyara a babban yankin kasar Sin

cri

A ran 28 ga wata da safe, Chiang Pin-kun, mataimakin shugaban jam'iyyar Koumintang ta Taiwan ya shugabanci wata kungiyar wakilai 34 zuwa birnin Guangzhou na babban yankin kasar Sin domin yin ziyarar kwananki 5 a babban yankin. Wannan ne karo na farko da jam'iyyar KMT ta kafa kungiyar wakilanta domin kawo wa babban yankin kasar Sin ziyara bayan ta je tsibirin Taiwan a shekarar 1949.

Kafin ya tashi daga Taiwan, Chiang Pin-kun ya ce, loakcin da suke yin ziyara a babban yankin kasar Sin, za su tuna da Sun Yat-sen a birnin Nanjing. Ban da wannan, kungiyar da hukumomin da abin ya shafa na babban yanki za su tattauna ko za su yi musayar ra'ayoyi kan wasu matsalolin ciniki da na tattalin arziki da ke kasancewa a tsakanin Taiwan da babban yankin. (Sanusi Chen)