Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-01-26 18:05:02    
Mu'amalar tsakanin jama'ar gabobi biyu na Zirin Taiwan a shekarar bara ta sami sabon ci gaba

cri
Wakilin Rediyon Kasar Sin ya sami labari cewa , A ran 26 ga watan nan a birnin Beijing , Li Weiyi , kakakin Ofishin kula da harkokin Taiwan na Majalisar gudanarwa ta kasar Sin ya bayyana cewa , a shekarar 2004 , ma'amalar tsakanin jama'ar gabobi biyu na Zirin Taiwan a fannoni daban daban ta sami sabon ci gaba.

Mr. Li ya yi wannan bayyani ne a gun taron manema labarun da aka saba yi a wannan rana. Ya ce , a wannan shekara , babban yankin kasar Sin zai ci gaba da sa kaimi kan mu'amalar jama'ar gabobi biyu da musaye-musayen dake fannin tattalin arziki da al'adu tare da babban sahihanci da iyakacin kokari kuma kamar yadda ya yi a da . Kuma babban yankin zai samar da wata damar farfado da tattaunawa da shawarwari cikin hanzari bisa ka'idar kasar Sin daya tak.(ADO)