Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-11-07 17:23:11    
An shirya taron manyan jami'ai a karo na 7 na dandalin tattaunawar hadin kai a tsakanin Sin da Afirka a birnin Sharm el-sheik na kasar Masar

cri

An shirya taron manyan jami'ai a karo na 7 na dandalin tattaunawar hadin kai a tsakanin Sin da Afirka a birnin Sharm el-sheik na kasar Masar a ran 6 ga wata, an shirya wannan taro ne domin share fage ga taron ministoci a karo na hudu na dandalin tattaunawar hadin kai a tsakanin Sin da Afirka, wanda za a shirya bayan kwanaki biyu.

Wannan taron manyan jami'ai ya zartas da shirin ajandar taron ministoci. Ban da wannan kuma an zartas da shirin rahotannin 'sanarwar Sharm el-sheik', da 'shirin daukar matakai daga shekarar 2010 zuwa 2012 na Sharm el-sheik', wadanda za a gabatar da su a gun taron ministoci da za a shirya domin dudduba su, haka kuma za a sanar da su a gun taron ministoci. Kasar Sin ta gabatar da rahoto kan aikin gaba dangane da taron koli na Beijing na dandalin tattaunawar hadin kai a tsakanin Sin da Afirka.(Danladi)