Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-09-28 21:37:55    
Manema labaru na kasashe masu tasowa sun yabawa ci gaban da kasar Sin ta samu

cri

Ran 27 ga wata, manema labaru 89 daga kasashe ko yankuna 53 na Asiya, da Afirka, da Latin Amurka sun sauka birnin Beijing, wadannan manema labaru daga kasashe masu tasowa za su ba da rahotanni kan ayyukan bikin taya murnar cika shekaru 60 da kafuwar sabuwar kasar Sin.

A wannan rana da yamma, manema labaru sun kai ziyara ga cibiyar watsa labaru ta bikin. Kafin wannan kuma, yawancinsu sun riga sun kai ziyara ga birnin Shanghai, da lardin Jiangsu, da lardin Guangdong. A wannan rana, mataimakin babban edita na jaridar Al Ahram ta kasar Masar ya ce, tattalin arzikin kasar Sin yana bunkasuwa cikin sauri sosai, haka ma a aikin gona, da masana'antu da sauran fannoni, kasar Sin ta samu ci gaban da ke jawo hankalin kasashen duniya sosai.

 

Manema labaru sun nuna cewa, bunkasuwar kasar Sin tana hade da moriyar kasashe daban daban, kuma suna fatan kasar Sin za ta samu ci gaba ma fi kyau a nan gaba. [Musa Guo]