A ran 13 ga wata, a birnin Beijing, firayim ministan kasar Sin Wen Jiabao ya nuna cewa, ko za a ci gaba da yin shawarwari tare da Dalai lama wani batu ne da ya danganci sahihancin zuciyarsa.
Wen Jiabao ya furta haka ne a lokacin da ya yi wata ganawa da manema labaru bayan kammala taron majalisar wakilan jama'ar kasar Sin.
Wen Jiabao ya nuna cewa, Tibet wani bangare ne na kasar Sin wanda ba za a iya raba shi da kasar ba, batun Tibet batu ne na harkokin gidan kasar Sin, bai dace kasashen waje su sa hannu cikin batun ba. Gwamnatin kasar Sin ta kan bayyana manufarta game da Dalai lami a fili, wato idan Dalai lama ya yi watsi da ayyukan kawo baraka, kasar Sin tana son yin shawarwari tare da wakilansa.
Wen Jiabao ya nuna cewa, Dalai lama wani 'dan siyasa ne mai gudun hijira, kuma akwai cikkakar shaidar hakan. Gwamnatin da suka kafa a birnin Dharmsala tana tsoma siyasa a cikin harkokin addinin Budda, kuma gwamnati ce da ke karkashin jagoranci Dalai lama.(Abubakar)
|