Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-03-12 19:41:45    
Sin ta nemi majalisar dokokin Amurka da ta daina amfani da batun Tibet wajen tsoma baki cikin harkokin gidanta

cri

Kwanan baya, majalisar wakilan Amurka ta zartas da wani shirin kudurin da ya shafi Tibet, kuma kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin, Mr.Ma Zhaoxu ya bayyana a ranar 12 ga wata a nan birnin Beijing cewa, Sin ta riga ta bayyana rashin jin dadinta ga Amurka, ta kuma nemi majalisar dokokin Amurka da ta gyara kuskurenta nan da nan, kuma ta daina yin amfani da batun Tibet wajen tsoma baki cikin harkokin gida na Sin, kada ta yi abin da zai lalata huldar da ke tsakanin Sin da Amurka.

An ce, kwanan baya, majalisar wakilan Amurka ta zartas da wannan kuduri, inda ba gaira ba dalili ta yi suka kan manufar gwamnatin Sin game da Tibet, har ma ta yi kirari ga Dalai Lama wanda ya dade yana ayyukan jawo baraka ga kasar Sin.

A yayin da yake amsa tambayoyin wakilinmu a gun taron manema labarai, Mr.Ma Zhaoxu ya jaddada cewa, kudurin ya yi biris da ainihin gaskiya, kuma ya saba wa ka'idoji na huldar da ke tsakanin kasa da kasa, ya kuma tsoma baki cikin harkokin gida na kasar Sin. Gwamnatin kasar Sin da jama'arta na nuna kyama sosai kan hakan.(Lubabatu)