Ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwa ta kasar Sin ya bayar da wani labari bisa ikonsa daga babban ofishin ba da jagoranci wajen yaki da bala'in girgizar kasa da ceto ta majalisar gudanarwa ta kasar Sin cewa, ya zuwa karfe 12 na ranar 11 ga wata, an tabbatar da cewa, mutane dubu 69 da dari 2 da 25 sun mutu, a yayin da mutane dubu 17 da dari 9 da 39 suka bace a sakamakon girgizar kasa a gundumar Wenchuan ta lardin Sichuan na kasar Sin.
Gwamnatoci daban daban na kasar Sin sun bayar da kudin Sin Yuan biliyan 64.4, al'umomi daban daban na kasar Sin sun bayar da kudin kyauta da yawansu ya kai kudin Sin Yuan biliyan 59.2, an riga an bayar da biliyan 23.8 daga cikinsu ga yankunan girgizar kasa.(Danladi)
|