2020-11-11 10:52:43 cri |
Kakakin rundunar sojojin Najeriya Benard Onyeuko, ya ce, an kashe mayakan na Boko Haram ne a ranar Litinin a musayar wutar da suka yi da mayakan a kauyen Buni Gari, dake karamar hukumar Gujba a jahar Yobe dake shiyyar arewa maso gabashin kasar, ya tabbatar da hakan.
Onyeuko ya ce, akwai kuma wasu mayakan 'yan ta'addan masu yawa da suka samu raunukan harbin bindiga a lokacin musayar wutar, a lokacin da suka yi yunkurin shiga kauyen na Buni Gari inda yunkurin nasu ya ci tura.(Ahmad)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China