2020-11-10 14:23:23 cri |
Karkashin dandalin na FOCAC, an daga huldar da ke tsakanin kasashen Afirka da Sin zuwa huldar abokantaka da hadin gwiwa daga dukkan fannoni bisa manyan tsare-tsare. Ya zuwa shekarar 2019, jimilar jarin da kasar Sin ta zuba a kasashen Afirka kai tsaye ta kai dalar Amurka biliyan 49.1 baki daya, wadda ta karu kusan sau 100 bisa ta shekarar 2000. Sa'an nan kuma, jimilar kudaden ciniki a tsakanin Sin da Afirka ta kai dalar Amurka biliyan 208.7, wanda ya karu da sau 20 bisa na shekarar 2000. A shakaru 11 a jere ne kasar Sin ta kasance abokiyar ciniki mafi girma ta Afirka.
Shekarar 2021 mai zuwa, shekara ce ta cika shekaru 50 da kulla huldar jakadanci a tsakanin Nijeriya a Sin. Don haka a cewar Bukola Ogunsina, kamata ya yi Nijeriya ta yi amfani da wannan dama, wajen gaggauta aiwatar da sakamakon da aka samu a yayin taron koli na Beijing, da habaka hadin gwiwar cin moriyar juna a tsakanin kasashen 2, a kokarin ciyar da huldar da ke tsakaninsu gaba. (Tasallah Yuan)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China