2020-11-09 14:23:08 cri |
Rukunin likitoci na Sin a wannan karo ya kunshi membobi 9, wadanda suke kula da ilmin bada jinya ga mutanen da suka kamu da cututtuka masu tsanani, da cututtuka masu yaduwa, da bada jinya ga marasa lafiya, da magance cututtuka da sauransu, kuma za su shiga asibitocin kasar Gambiya don bada horo, da bada jinya ga mutane masu fama da cutar COVID-19.
Haka zalika kuma, rukunin likitocin na Sin da zai yi aiki a kasar Gambiya karo na 4, zai tashi tare da rukunin likitoci na Sin mai aikin gajeren lokaci zuwa kasar ta Gambiya, don gudanar da ayyukan likitanci har na tsawon shekara daya. (Zainab)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China