Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Jami'in Najeriya: Zanga-zangar baya-bayan da aka yi a kasar na iya dawo da COVID-19
2020-10-27 19:30:34        cri
Sakataren gwamnatin tarayyar Najeriya kana shugaban kwamitin da shugaban kasar ya nada kan yaki da annobar COVID-19, Boss Mustapha ya bayyana fargabar cewa, zanga-zangar neman yi wa rundunar 'yan sandan kasar gyaran fuska ta baya-bayan nan a kasar, na iya dawo da annobar COVID-19.

Boss Mustapha wanda ya bayyana haka, yayin wani taron manema labarai da aka shirya jiya Litinin ya ce, a cikin makonni biyu da suka gabata, an gudanar da gagarumar zanga-zanga a sassa daban-daban na kasar, ba tare da martaba ka'idojin yaki da annobar COVID-19 ba.

Ya ce, baya ga yadda yanayin tsaron kasar ya shafi tattalin arziki da zaman takewar al'umma, gangamin da aka gudanar da ma yadda masu boren suka rika balle manyan dakunan ajiyar kayayyaki, da gidaje da wawashe dakunan ajiyar kayayyaki da matasa suka yi, ya jefa kasar cikin hadarin sake bullar kwayar cutar.

A cewar cibiyar kandagarkin yaduwar cututtuka ta kasar(NCDC), an tabbatar sabbin mutane 119 da suka kamu cutar a ranar Litinin, adadin da ya kai 62,111 gaba daya a kasar. Akwai mutane 1,132 da cutar da halaka, baya ga 57,571 da suka warke daga cutar, tun barkewarta a karshen watan Fabrairu.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China