2020-10-02 18:32:40 cri |
A matsayin kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kasar Sin ta yi bakin kokarinta, sannan ta samu nasarori da dama a fannin shimfida daidaiton jinsi. Kawo yanzu, Sin ta kafa wani ingantaccen tsarin tabbatar da hakkokin mata, ciki har da zartas da dokoki sama da 100.
Domin kara goyon-bayan ci gaban harkokin matan duniya, shugaba Xi ya sanar da wasu matakan da kasarsa za ta dauka nan da shekaru biyar dake tafe, ciki har da kara samar da kyautar kudi da yawansa ya kai dala miliyan 10 ga hukumar mata ta MDD , da ci gaba da bayar da lambar yabo ta Sin da UNESCO kan aikin bada ilimi ga yara mata da 'yan mata. Kana shugaba Xi yana kira da a sake gudanar da taron kolin kasa da kasa kan harkokin mata nan da shekaru biyar masu zuwa, al'amarin da ya shaida cewa kasar Sin tana da hangen nesa da maida hankali sosai kan bunkasuwar harkokin mata a duniya.
A halin yanzu cutar COVID-19 na ci gaba da addabar duniya, akwai bukatar raya duniya da babu bambancin ra'ayi ko wariyar da ake nunawa mata. In dai an cimma wannan buri, za'a kara samun wayewar kai, har ma zamantakewar al'umma za ta ci gaba da kyautata.(Murtala Zhang)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China