![]() |
|
2020-09-03 21:18:07 cri |
Sanin kowa na cewa, batun Xinjiang, batu ne da ke shafar yaki da 'yan ta'adda, da yin adawa da kawo baraka ga kasar Sin. A don haka, bai shafi hakkin dan Adam, ko al'umma, ko addini ba. Sakamakon jerin matakan da gwamnatin kasar Sin take dauka domin yaki da ta'addanci da kawar da tsattsauran ra'ayi a jihar, ya sa aka samu kwanciyar hankali da wadata a wurin. Al'ummomin Xinjiang sun ci gajiyar bunkasar jihar sosai, inda kuma ake kyautata ba da tabbacin zaman al'ummar kasa, da kare dukkan hakkokin al'ummomin jihar.
A daren ranar 1 ga wata ne jihar ta Xinjiang ta samu farfadowa daga dukkan fannoni yayin da take ci gaba da dakile da kandagarkin cutar COVID-19. Kafofin yada labaru na wurin sun ruwaito cewa, yanzu haka, rukunin farko na masu yawon shakatawa suna kan hanyar zuwa jihar. Kasar Sin tana maraba da dukkan mutanen da suke kula da jihar Xinjiang da su ziyarci jihar. Tabbs karyar da aka yi kan batun Xinjiang da kuma bata sunan kasar Sin ba za su yi nasara ba, saboda shaidun dake bayyane a zahiri. (Tasallah Yuan)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China