Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Aminu Hussaini Adamu Gumel: Noma tushen arziki
2020-07-28 14:33:02        cri


Aminu Hussaini Adamu Gumel, wanda aka fi sani da suna Aminu 1 Naira, wani dalibin Najeriya ne wanda a yanzu haka yake karatun digiri na biyu a jami'ar koyon aikin gona ta kasar Sin dake Beijing.

A zantawarsa da Murtala Zhang, Aminu 1 Naira ya bayyana cewa, ko da yake bai jima da zama a kasar ta Sin ba, amma ya ganema idanunsa babban ci gaban da kasar ta samu a fannoni daban-daban, har ma ya ziyarci wuraren yawon shakatawa da na tarihi da dama a kasar, inda ya ji dadin yadda mutanen kasar Sin ke kulla zumunci da baki 'yan kasashen waje, musamman bakake fata.

Aminu 1 Naira, wanda a yanzu haka yake gudanar da ayyukan gwaji a fannin aikin gona a karkashin jagorancin malaman jami'arsa a lardin Hebei na kasar Sin, ya ce kasar Sin ta samu babban ci gaba wajen gudanar da aikin gona, ganin yadda take da fasahohi gami da na'urorin zamani masu tarin yawa. Aminu ya kuma bayyana fatansa ga matasan Najeriya don su bada muhimmanci kan ayyukan gona, saboda a cewar malam Bahaushe, noma tushen arziki.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China