Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Shigar Sin cikin yarjejeniyar AfCFTA ya taimaka wajen cimma nasarar manufar
2020-07-23 10:46:03        cri
Kwararre a fannin hada hadar cinikayyar kasa da kasa Francis Kofi Korankye-Sakyi, ya ce muhimmiyar rawar da kasar Sin ta taka a fannin bunkasar tattalin arzikin nahiyar Afirka, da ci gaban siyarsar nahiyar, ya sanya Sin din zama muhimmin jigo, wajen tabbatar da cimma nasarar yarjejeniyar cinikayya maras shinge ta Afirka ko AfCFTA a takaice.

Mr. Korankye-Sakyi, wanda ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ya ce karkashin dadadden tsarin hadin gwiwar ta da Afirka, Sin ta taka rawar gani, wajen ingiza cimma nasarar ajandar nahiyar ta nan da shekarar 2063, kudurin da shi ne ya haifar da yarjejeniyar ta AfCFTA.

Korankye-Sakyi, wanda kuma shi ne babban jami'in ofishin Afirka na tsara manufofin zuba jari a kasar Ghana, ya kara da cewa, Sin ta saukaka cudanyar ta da Afirka, ta hanyar goyawa nahiyar baya, da samar mata da hidimomi bisa tsari da bin doka. Ta kuma samar da kudaden gudanar da muhimman ayyuka ba tare da gindaya irin sharuddan da kasashen yamma ke sanyawa kasashen nahiyar ba.

A nasa tsokaci, shugaban kamfanin fasaha na mPedigree dake birnin Accra Mr. Bright Simons, ya yi hasashen cewa, saurin kafa kyakkyawar alakar tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, ya baiwa Sin din damar bunkasa hada hadar cinikayya da nahiyar, sama da sauran abokan takarar ta karkashin sabuwar yarjejeniyar ta AfCFTA. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China