![]() |
|
2020-07-20 10:04:09 cri |
Cikin rahotonta na baya-bayan nan da ta fitar a jiya, cibiyar ta ce adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar a nahiyar ya karu daga 683,905 da yammacin ranar Asabar, zuwa 701,573 ya zuwa safiyar jiya Lahadi.
Cibiyar ta kara da cewa, adadin wadanda cutar ta yi sanadin rayukansu shi ma ya karu, zuwa 14,937.
Har ila yau, cibiyar ta Africa CDC, ta ce tuni mutane 369,120 daga cikin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar, suka warke.
Yayin da ake tsaka da fama da yaduwar cutar a fadin nahiyar, kasashen da ta fi shafa sun hada da Afrika ta kudu da Masar da Nijeriya da Ghana da Algeria da Morocco da kuma Kamaru. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China