Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Dr. Sheriff Ghali Ibrahim: Kasar Sin tana bakin kokarinta wajen kare hakkin al'ummarta
2020-07-14 13:19:12        cri


Dr. Sheriff Ghali Ibrahim, malami ne dake koyarwa a sashin kimiyyar siyasa da huldar kasa da kasa a jami'ar Abuja ta Najeriya. A yayin zantawarsa da Murtala Zhang, Dr. Sheriff ya jaddada cewa, gwamnatin kasar Sin tana bakin kokarinta wajen kare hakkin dan Adam, ciki har da maida hankali kan kare tsaro da lafiyar al'umma, da taimaka musu wajen samun ci gaba.

Dangane da batutuwan da suka shafi yankunan Hong Kong da Taiwan da Tibet da kuma Xinjiang, Dr. Sheriff ya ce dukkan sassan mallakin kasar Sin ne, wadanda ba za'a iya balle su daga kasar ba. Kuma a iya saninsa, babu wani batun tauye hakkin dan Adam a wadannan wurare, sai dai kawai akwai wasu kasashen yammacin duniya wadanda suke amfani da batun hakkin al'umma domin fatattakar gwamnatin kasar Sin, da kuma shafa mata bakin fenti, domin kawo tsaiko ga ci gaban kasar.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China