![]() |
|
2020-07-08 10:34:25 cri |
Cikin wata sanarwar da ya fitar, shugaban rundunar sojin saman kasar Sadique Abubakar, ya shaiwada manema labarai hakan jiya Talata, yana mai cewa, hare-haren na ranar Litinin, daya ne daga matakan da ake dauka, na kakkabe yankin daga ayyukan 'yan bindiga, da 'yan fashin shanu, da masu garkuwa da mutane, da ma sauran masu aikata laifuka dake addabar al'ummar yankin.
Sadique Abubakar, ya kara da cewa, da yake dajin Kagara ya dangana zuwa janhuriyar Nijar, dakarun Najeriyar na aiki kafada da kafada da takwarorin su na Nijar, don tabbatar da 'yan bindiga ba su tsere ta kan iyakokin kasa da kasa yayin da ake fatattakar su ba. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China