Kakakin Sin: Duk wani yunkuri na neman lalata alakar dake tsakanin Sin da Afrika ba zai yi nasara ba
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Zhao Lijian, ya sanar a yau Litinin cewa, Afrika mahimman 'yan uwa ne ga kasar Sin dake da kyakkyawar nasaba iri daya. A wannan yanayi da ake ciki na barkewar annoba, Sin da Afrika suna aiki tare domin tinkarar annobar. Duk wani yunkuri na neman lalata alakar dake tsakanin Sin da Afrika saboda mummunan kudiri ba zai taba yin tasiri ba kuma ba zai yi nasara ba. (Ahmad Fagam)
Labarai masu Nasaba