![]() |
|
2020-05-09 21:57:49 cri |
Ta ce abun da kowa ya sani ne cewa, a watan Oktoban 1971, zauren MDD na 26, ya amince da kuduri mai lamba 2758, dake bayyana gwamnati Jamhuriyar Jama'ar Kasar Sin, a matsayin halaltacciyar gwamnatin dake wakiltar kasar Sin.
Ta ce manufar kasar Sin daya tak a duniya kuma Taiwan wani yanki nata ne da ba zai iya ballewa ba, abu ne da kasashen duniya suka amince da shi. Kuma MDD ta sha nanata cewa, tana son a rika tafiyar da batutuwan da suka shafi Taiwan bisa kudurin mai lamba 2758, inda Hua ta kara da cewa, a matsayinta na hukumar dake karkashin MDD, ya kamata WHO ta kiyaye kudurin babban zauren majalisar. (Fa'izaMustapha)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China