2020-05-06 19:54:26 cri |
Tanoh Aristophane, likita ne a asibitin koyarwa na Treichville, inda aka kebe musamman domin samar da jinya ga masu cutar Covid-19, ya kuma bayyana cewa, zuwan jami'an lafiya na kasar Sin ya karfafa wa ma'aikatan lafiya na Cote d'Ivoire niyyar samun galaba a kan cutar, kuma fasahohin kasar Sin za su taimaka wa Cote d'Ivoire, wajen shawo kan cutar cikin hanzari.
Bisa goron gayyatar gwamnatin Cote d'Ivoire, ayarin jami'an lafiya na kasar Sin ya isa birnin Abijan, a ranar 30 ga watan da ya wuce. (Lubabatu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China