![]() |
|
2020-04-28 12:03:17 cri |
Ministan kudi na kasar Ipumbu Shiimi, ya ce gwamnati za ta bayar da dalar kasar miliyan 400, yayin da hukumar kula da jin dadin jama'a za ta bayar da dalar 250, domin taimakawa ma'aikata rike ayyukansu.
Ministan ya ce gwamnati na amfani da tallafin domin tabbatar da kasar ta ceci yiwuwar rashin aikin yi a nan gaba.
Ya kara da cewa, tallafin wani bangare ne na shirye-shiryen da aka gabatar domin ceton tattalin arzikin kasar daga durkushewa saboda kullen.
Jami'ar zartarwa ta hukumar kula da jin dadin jama'a ta kasar Milka Mugunda, ta ce hukumar ta bada tallafin ne domin tabbatar da kula da yanayin zamantakewar matalauta da masu rauni. (Fa'iza Mustapha)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China