Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
COVID-19: Shugaba Buhari ya bukaci 'yan Najeriya su zauna a gida ya bada tabbacin bayar da karin tallafi
2020-04-12 17:16:28        cri
A kokarin gwamnatin Najeriya na yaki da annobar COVID-19, shugaban kasar Muhammadu Buhari, ya bukaci jama'ar kasar dasu cigaba da zama a cikin gidajensu tare da wanke hannuwa a kowane lokaci bisa ga shawarwari da kwararrun masana kiwon lafiya ke bayarwa domin samun kariya daga annobar cutar numfashi ta COVID-19.

Cikin wata sanarwar da mataimaki na musamman ga shugaba Buhari kan kafafen yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar yace, ya zama tilas a bukaci al'ummar kasar dasu kara takaita zirga zirga a duk inda suke a fadin kasar domin mutunta shawarwarin kwararrun masana kiwon lafiya.

Sanarwar tace, mutanen da suka fi fama da matsin rayuwa a kasar, gwamnati ta sanar da daukar matakai daban daban domin tallafa musu, daga ciki akwai fitar da ton 70,000 na hatsi da gwamnatin tarayya ta adana a rumbunan ajiyarta domin rabawa ga mutane masu tsananin bukata, da kuma bada tallafin kudade ga masu karamin karfi, kuma gwamnatin tarayyar kasar, da jihohi da kuma kananan hukumomi zasu cigaba da bayar da tallafin ga jama'a.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China