2020-04-12 17:06:19 cri |
Jakada Cui ya bayyana hakan ne a yayin hira da ya yi ranar 3 ga watan Afrilu da Ian Bremmer a shirin Gzero World, wacce tashar talabijin ta Amurka ta watsa a ranar Asabar.
Ya ce wannan babbar matsala ce da ta shafi kowa da kowa, jakadan yayi watsi da zarge zargen da wasu 'yan siyasar yammacin duniya ke yi cewa kasar Sin tana da wata manufar siyasa wajen tallafawa sauran kasashen duniya don yaki da annobar.
A cewarsa babban abin da muke taimakawa sauran kasashe shi ne sabo da dukkan al'ummar duniya makomarsu daya ce. Yace kasar Sin ba zata taba zama cikin kwanciyar hankali ba idan dukkan kasashen duniya suna fama da yaki da annobar, asali ma muna taimakon kanmu ne ta hanyar taimakawa sauran kasashe, in ji jakadan na Sin.
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China