![]() |
|
2020-01-03 10:04:08 cri |
Wasu majiyoyin tsaron sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, daga cikin wadanda aka kashe sun hada da maharan da kuma wani jandarma.
Harin na zuwa ne, yayin da shugaban kasar Burkina Faso Roch Marc Christian Kabore, ke yiwa 'yan kasar jawabi a ranar Talata da dare, inda ya bayyana tabbacin samun galaba a matsalar ta'addancin dake addabar kasar.
Daga shekarar 2015 zuwa wannan lokaci, hare-haren ta'addanci sun halaka rayukan mutane sama da 700, ciki har da sojoji 200, baya ga dubban mutane da suka rasa matsugunansu a cikin kasar.(Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China