2019-12-20 19:18:52 cri |
A nasa bangare, Mr. Sassou ya ce kasarsa na martaba kawance dake tsakaninta da Sin. Har ila yau, al'ummar kasar na jinjinawa tallafin da Sin ke samarwa kasar a tsawon lokaci, musamman irin taimakon jin kai da Sin din ta samarwa Congo a baya bayan nan, sakamakon ambaliyar ruwa da ta mamaye wasu sassan kasar.
Shugaba Sassou ya kara da cewa, Congo za ta ci gaba da shiga a dama da ita, cikin shawarar "Ziri daya da hanya daya", tana kuma burin karfafa hadin gwiwa mai inganci a muhimman sassa, ciki hadda fannin noma, da samar da ababen more rayuwa, da kayayyakin bunkasa masana'antu. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China