![]() |
|
2019-12-02 10:28:27 cri |
A cewar hukumar, ya zuwa karshen watan Oktoban wannan shekara, akwai mutane 958,000 dake dauke da kwayar cutar a kasar Sin, bayan rahoton da ke nuna cewa, akwai sabbin mutane 131,000 da suka kamu da cutar a watanni 10 na farkon wannan shekara.
Hukumar ta NHC ta tsara matakan da suka dace na hana yaduwar cutar ta hanyar jima'i, babbar hanyar da a halin yanzu ake yada cutar a kasar Sin da magance yadda mahaifiya ke yada cutar ga jaririn da ke cikinta.
Yanzu haka hukumar ta ce, an gano lardunan da cutar ta fi kamari da yankunan dake fama da talauci da ma matasa baligai da dalibai, a matsayin aiki mai muhimmanci na kawar da wannan cuta.
Hukumar ta lashi takwabin karfafa matakai na ilimantar da jama'a game da nauyin dake wuyansu a bangaren kiwon lafiya da hukunta masu keta doka da manyan laifukan da suke da nasaba da yada cutar AIDS, da matakan kariya gami da magance cutar da makamantansu.(Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China