2019-09-14 17:04:45 cri |
Stephane Dujarric, ya ce, yawan mutanen da suke bukatar taimakon jin-kai ya karu da kaso 22 tun daga farkon shekarar da muke ciki, kana kuma kaso 20 na jama'ar kasar Mali na rayuwa bisa tallafin kasa da kasa. Ya ce zuwa karshen watan Yuli, adadin mutanen da suka rasa matsugunansu a Mali ya tasam ma dubu 170.
Dujarric ya ce, har yanzu akwai mutane sama da dubu dari biyar a Mali wadanda ke rayuwa cikin matsanancin hali na rashin isasshen abinci.
Tun daga watan Maris din shekarar 2012 zuwa yanzu, yanayin siyasa da tsaro gami da fadace-fadace tsakanin kabilu a Jamhuriyar Mali na dada ta'azzara.
Bisa alkaluman da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar a watan Fabrairun bana, yawan sojojin majalisar na wanzar da zaman lafiya da suka rasa rayukansu a Mali a shekara ta 2018 ya fi yawan sojojin majalisar da suka mutu a sauran kasashe.(Murtala Zhang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China