2019-09-08 16:56:23 cri |
Rahotanni sun ce, a cikin 'yan kwanakin da suka wuce, akwai mutanen da suka lalata gine-gine da na'urorin hanyar dogo, a ranar 7 ga wata kuma, akwai wadanda suka hana gudanar ayyuka a filin jiragen sama na kasa da kasa na Hong Kong.
Bugu da kari kuma, sanarwar ta nuna cewa, kafin hakan, kotu ta riga ta ba da umurnin haramta duk wani yunkurin hana ayyukan filin jiragen sama da hanyar dogo. Gwamnatin yankin ta yi kira ga mazauna cewa, bai kamata su nuna ra'ayoyinsu ta hanyar keta doka ba, kuma dole ne su yi la'akari da iko da bukatun matafiya da na sauran mutanen yankin. (Bilkisu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China