![]() |
|
2019-06-20 09:30:15 cri |
Ministocin harkokin wajen kasashe mambobin AU 55, a taron majalisar zartaswar AU da za su gudanar a ranar 4 zuwa 5 ga watan Yulin a Niamey, ana sa ran za su bayar da shawarwari game da yadda za'a aiwatar da yarjejeniyar ciniki maras shinge gabanin taron kolin shugabannin gwamnatocin AU karo na 12 wanda za'a gudanar a ranar 7 ga watan Yuli, in ji sanarwar AU.
Shugaban gudanarwar kungiyar ta AU Moussa Faki Mahamat ya ce, yarjejeniyar AfCFTA ta kasance a matsayin wani muhimmin ginshiki na burin da AU ke da shi wajen cimma nasarar bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'ummar nahiyar Afrika.
Yarjejeniyar ta AfCFTA, wacce kasashen Afrika 44 suka rattaba hannu a lokacin kaddamar da ita a Kigali, babban birnin kasar Rwanda, a watan Maris na shekarar 2018, tana fatan ganin an samar da wani tsarin cinikin bai daya a nahiyar ba tare da sanya kudaden haraji ba da nufin bunkasa harkokin kasuwancin kasashen, da bunkasa harkokin cinikayya a tsakanin kasashen Afrika, da bunkasuwar masana'antu da samar da guraben ayyukan yi. (Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China