Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sojojin rundunar kawance ta MNJTF sun kashe 'yan ta'adda 20 a Nijeriya
2019-06-04 09:27:13        cri
Akalla 'yan ta'adda 20 aka kashe biyo bayan matakin soji da sojojin kawance na kasashen Nijeriya da Chadi da Kamaru da Niger suka dauka.

Kakakin rundunar kawancen ta MNJTF, Timothy Antiga, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, an kashe 'yan ta'addan ne yayin samamen da aka kai yankunan Arege da Malkonory da kuma Tumbum Rego.

Ya ce aikin wani bangare ne na matakin soji da aka dauka domin fatattakar mayakan IS daga yankin tafkin Chadi.

Sai dai, ya ce jami'an rundunar 4 sun samu rauni yayin bata kashin da aka yi tsakaninsu da 'yan ta'addan, kuma tuni aka garzaya da su asibiti don samun kulawa.

Jami'in ya ce rundunar ta kuduri niyyar cimma burinta, yana mai kira ga mutanen yankin su ci gaba da ba su goyon baya.

A watan Fabrerun bana ne rundunar kawance ta MNJTF, ta kaddamar da sabon aikin fatattakar mayakan Boko Haram daga yankin tafkin Chadi. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China