2019-06-01 15:20:56 cri |
Kakakin hukumar reshen jihar Lagos Bisi Kazeem, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya samu kwafinta, inda ya ce matakan da aka dauka, sun yi daidai da manufar hukumar, na gudanar da sintirin musamman yayin bukukuwa, da nufin rage cunkoso, da hadurran ababen hawa ko rasa rayuka.
Kazeem ya kara da cewa, burin su shi ne tabbatar da an gudanar da bukukuwan karamar sallah lami lafiya, cikin tsaro da zirga zirgar mutane da ababen hawa yadda ya kamata a daukacin sassan kasar.
Jami'in ya kuma yi kira ga masu ababen hawa, da su baiwa jami'an hukumar ta FRSC da sauran jami'an tsaro hadin kai, ta yadda za su gudanar da ayyukan su yadda ya kamata.
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China