![]() |
|
2019-05-27 20:37:43 cri |
Mataimakin darekta a sashen kula da walwalar yara a ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar, Ni Chunxia ya shaidawa taron manema labarai cewa, a shekarar 2019 da muke ciki, a karon farko ma'aikatar ta kebe Yuan miliyan 400, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 58, daga asusun tallafawa mutane dake fama da matsalar kudi, domin kula da wadannan yara.
Ni ya ce, za a yi amfani da asusun ne wajen tattara shaidu kan wadanda ke neman taimako,tantance yadda ake kula da yaran, da sake bibbiyar wadannan yara da ziyartar yaran dake bukatar taimako, musamman wadanda ke zaune a yankuna masu fama da talauci.(Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China