A wannan mako, za ku ji wata hira da abokin aikinmu Murtala Zhang ya yi da Abubakar Abdallah daga jihar Kaduna a tarayyar Najeriya, wato ma'aikaci a kamfanin sadarwa da fasahar watsa labarai na kasar Sin wato Startimes dake birnin Beijing, inda ya yi tsokaci game da irin zaman rayuwarsa a nan kasar Sin da yanayin aikinsa har ma da irin kalubalolin da yake fuskanta. Ga dai yadda hirar tasu ta kasance.