Xi ya taya Steinmeier murnar sake zabarsa shugaban Jamus
2022-02-14 10:38:41 CRI
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taya Frank-Walter Steinmeier murnar sake zabarsa a mukamin shugaban tarayyar Jamus.
A sakon taya murnar da ya aika masa, Xi ya bayyana cewa, a wannan shekara ake bikin cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Jamus.
Shugaba Xi yana dora muhimmanci kan ci gaban huldar dake tsakanin Sin da Jamus, kuma a shirye yake ya yi aiki tare da Steinmeier domin bunkasa huldodin dake tsakanin kasashen Sin da Jamus daga dukkan fannoni. (Ahmad)